Sunday, August 12, 2018

[SIYASA] NI DA BUHARI DAN JUMMA NE DA DAN JUMMAI - GANDUJE





Ni Da Buhari Danjuma Ne Da Danjummai, Cewar Gwamna Ganduje

Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje OFR ya ja Hankalin 'Yan
Jam'iyyar APC Na Jihar Kano akan taba muhibbar duk wani wanda
yake Tafiyar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a Jihar Kano.
Gwamna ya bayyana haka ne yau a wajen Bikin Ranar Matasa ta
Duniya wanda aka Gabatar a dakin Wasa Na Sani Abacha dake
Kofar Mata inda yace Koda Shugaban Kasa Muhammadu Buhari
mutum yake kauna Amma baya kaunarsa to kada a zage shi domin da
shi da Muhammadu Buhari Danjuma ne da Danjimmai don haka kar
a zage shi.
Ya ja Hankalin Matasa akan wasu da ya ji suna zagin masu mukamai
a Gwamnatin Tarayya daga jihar Kano inda ya umarce su da su daina.
SSA Social Media II,Kano
Abubakar Aminu Ibrahim.



Danna Nan Domin Shiga Whatsapp Group Din Mu

No comments:

Post a Comment