Saturday, March 9, 2019

[LABARAI] KO KACHI KO KACHI KUKAN ZUCHI









GUSAULOADED ta yi shiri tsaf domin kawo wa dimbin masu karatun ta labarai, rahotanni da bayanan sakamakon zaben gwamnoni kai-tsaye.

Wannan zabe na gwamnoni da majalisar dokoki zai zama zaben zaben kai-da-halin-ka. Domin dai alamomi sun nuna cewa ba duk wanda Shugaba Muhammadu Buhari ya ce a zaba ne za a rufe ido a zabe shi ido rufe ba.

Shi kan sa Buhari ya furta cewa kowa ya zabe wanda ran sa ya kwanta masa. Wannan kuwa zai ba jama’a da dama damar huce-haushin su a kan wasu gwamnoni, musamman wadanda suka rika gajiyar da su kafin biyan su albashi da wadanda suka ki yarda a yi karin albashin.

Wani abin dubawa dangane da wannan zabe, shi ne ba a kowace jiha cwe gaba daya 36 za a yi zaben ba. Ba a yi zaben gwamna a jihohin Kogi, Osun, Ekiti da Ondo ba. Saboda gwamnonin da ke kai bas u cika shekara hudu a kan mulki ba. amma kuma za a yi zabukan majalisar dokoki a jihohin.
Jihohin da jama’a za su fi bada hankali a zaben gwamna sun hada da: Kano, Kaduna, Lagos, Akwa Ibom, Rivers da Taraba.

Akwai kuma Jigawa, Enugu da Imo da Gombe da Oyo da kuma Sokoto.

SOKOTO:

Wakilin mu ya ci karo da dandazon jagororin Jam’iyyar APC da magoya bayan su suna siyan Kuri’u a boye. Wani da ya tattauna da wakilin mu ya ce duk wadanda suke da katin zabe na dindindin ne ake biya wadannan kudade domin siyan kuri’un su.

Ya kara da cewa ana biyan daga naira 3000 zuwa har 700.

An samu wadannan masu rabon kudi ne cikin daren Juma’a zuwa wayewar asabar din yau.


KADUNA:

Jami’in hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa reshen jihar Kaduna Abdullahi Kaugama ya bayyana cewa za a yi amfani da na’urar tantance katin masu zabe ‘Card Reader’ har 3,008 a zabe a Kaduna.
Kaugama ya fadi haka ne da yake ganawa da manema labarai a ofishin hukumar dake unguwar Rimi a Kaduna ranar Juma’a.

Ya kuma jadadda cewa hukumar zabe za ta soke zaben da aka yi a rumfar da na’urar ‘Card Reader’ bai yi aiki ba.

” A dalilin haka muke kira ga mutane da su kwantar da hankulan su bi ma’aikatan mu sannu a hankali tare da tabbatar cewa na’urar ‘Card Reader’ na aiki kafin su jefa kuri’un su.

DAURA:

Da misalin karfe takwas na safiyar yau Asabar ne shugaban kasa Muhammadu Buhari tare da uwargidan sa Aisha suka nufi rumfar zabe 003 dake Gidan Niyam a Daura jihar Katsina domin jefa kuri’un su.

Da karfe 8:08 bayan an kammala tantance su shugaba Buhari tare da Aisha suka kada kuri’un su.

HOTUNA:












No comments:

Post a Comment